News

NUT TA KAI WA MALAM UBALE DAUKIN GAGGAWA

IMG 20260130 WA0037
IMG 20260130 WA0037

ƘUNGIYAR NUT TA KAIWA MALAM UBALE ADO DAUKIN GAGGAWA

Ƙungiyar Malaman makaranta ta Nigeria (NUT) reshen karamar hukumar Nassarawa ta kai wa malam Ubale Ado tallafin kuɗi a ranar Juma’a 30/1/2026 bisa iftila’in gobara da ta babbake masa gidansa.

IMG 20260130 WA0038

Shugaban ƙungiyar Comrade Nura Lawal tare da wasu jagororin kungiyar ne su ka mika wannan tallafi na ₦70,000 tare da jajanta masa . Lawal ya ƙara da cewa, iftila’in da ya samu malam Ubale Ado abun a tausaya masa ne, duba da yadda wutar ta babbake masa gidansa kusan gaba ɗaya .

Ubale Ado na ɗaya daga cikin ma’aikatan Nassarawa LGEA wanda ya ke aiki a sashen adana takardu(Registry).

Malam Ado ya yi godiya ga NUT bisa wannan tallafi da su ka kawo masa har gida.

Baba Comrade, E-magazine

30/1/2026

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *