Tinubu: Jihohi Sun Daina Fama da matsalar biyan Albashi, Gwamnoni Sun nemi a sabunta albashin ma’aikata zuwa mafi ƙarancin ₦100,000
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana gamsuwarsa da yadda harkokin kuɗi na gwamnatocin jihohi ke inganta, yana mai cewa jihohi da dama ba sa dogaro da tallafin gwamnatin tarayya wajen biyan albashi kamar da.
Shugaban ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da yake karɓar baƙuncin mambobin Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF), ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, a wata ziyarar gaisuwar Sallah da suka kai masa a gidansa da ke Lagos.
Da yake waiwayar tafiyarsa zuwa shugabancin ƙasa, Tinubu ya bayyana lokacin da ya gabaci zaɓen 2023 a matsayin ɗaya daga cikin mafi wahalar lokuta a rayuwarsa ta siyasa, wanda ya ƙunshi matsananciyar gwagwarmaya ta siyasa da shari’a.
“A lokacin, na fuskanci ƙalubalen neman zama Shugaban Ƙasar Nijeriya. Lamarin ya kasance mai wahala da ƙunci ga waɗanda suka tsaya tare da ni. Wasu sun ci gaba da riƙe imani, kuma maimakon kaucewa ƙalubale, na fuskance su kai tsaye,” in ji Shugaban.
Gwamnan Jihar Kwara ya kuma yi hasashen cewa ƙaramin albashin ƙasa zai iya kaiwa N100,000 nan gaba, idan har yanayin kuɗin jihohi ya ci gaba da inganta.
Shi ma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jam’iyyar APC kuma Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma, ya yaba da shugabancin Tinubu, yana mai bayyana sauye-sauyen tattalin arzikin da ya aiwatar a matsayin jajircewa mai ƙarfi da ta taimaka wajen daidaita ƙasar.
“Ka ceto Nijeriya daga bakin durkushewa zuwa wani mataki na daidaito da tsira,” in ji Uzodinma, yana ƙara da cewa gwamnonin sun tantance aikin Shugaban tare da ba shi kashi 100 cikin 100.
Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Murtala Sule Garo, ya wakilci Gwamna Abba Kabir Yusuf a taron.
Tinubu ya gode wa goyon bayan gwamnonin da mambobin jam’iyya waɗanda suka ci gaba da kasancewa masu biyayya duk da rashin tabbas kan manufofin da gwamnatinsa za ta aiwatar.
A cewarsa, Nijeriya ta kuɓuta daga barazanar durkushewar tattalin arziki, kuma tana fara ganin ribar manyan sauye-sauyen da gwamnatinsa ta gabatar.
“Maimakon durkushewa, Nijeriya ta tsira. Tattalin arziki ya farfaɗo kuma yana bunƙasa. Noma yana inganta, samar da abinci yana ƙaruwa, kuma ayyukan more rayuwa suna ci gaba a faɗin ƙasar,” in ji shi.
Shugaban ya yaba wa gwamnonin bisa taimakonsu wajen tabbatar da amincewa da haƙurin jama’a yayin aiwatar da sauye-sauyen da ya bayyana a matsayin masu wahala amma dole.
Ya ƙara da cewa alamomin tattalin arziki sun inganta sosai, yayin da ake farfaɗo da ayyukan gine-gine da aka bari a baya, sannan bangaren gidaje yana sake samun ci gaba.
“Ina farin ciki cewa jihohin da a baya suke dogaro da tallafin tarayya yanzu ba sa fama da biyan albashi. Wannan matsala ta kau,” in ji Tinubu.
Da yake magana a madadin gwamnonin, Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya kuma Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce cire tallafin mai da sauran sauye-sauyen kuɗi sun ƙarfafa ƙarfin tattalin arzikin jihohi.
Ya bayyana cewa jihohi da dama sun biya bashin albashi da fansho, sun rage nauyin bashi, tare da aiwatar da muhimman ayyukan more rayuwa da shirye-shiryen jin daɗin al’umma.
“Ina ganin ƙasar ta yi mamakin jajircewar Shugaban wajen aiwatar da wannan manufa, amma a yau ƙasar ta amfana sosai daga gare ta,” in ji AbdulRazaq.
Ya kuma sake jaddada yiwuwar ƙara ƙaramin albashi zuwa N100,000 idan yanayin kuɗin jihohi ya ci gaba da inganta.
