GARO: SABON SHAFIN SIYASAR KANO
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi murabus daga jam’iyyar NNPP, kuma komawarsa zuwa jam’iyyar APC abu ne da ya zama tabbatacce.
Tunda Mataimakin Gwamna, Aminu Abdussalam Gwarzo, ya ci gaba da kasancewa a NNPP, hakan ya haifar da bayyanannen gibi a matsayin Mataimakin Gwamna a sabon tsarin da ake shirin yi na sake jera siyasar Kano a karkashin mulkin APC.
Duba da yadda al’amura ke tafiya, wannan ne ya sa Murtala Sule Garo ya zama mabuɗin sake fasalin siyasar Kano.
Garo ɗan siyasa ne mai ƙarfi a matakin ƙasa-ƙasa (grassroots). Duk lokacin da ya bi titunan Kabo ko wasu daga cikin al’ummomin da ya taɓa, matasa maza da mata kan cika gefen hanya suna raira taken: “Sai Commander.”
Wannan laƙabi ba wai kawai alamar karamci ba ne, yana wakiltar suna da ya gina bisa jajircewar aikin al’umma, jagoranci mai tsauri da hangen nesa na siyasa da ya ɗaga shi daga mataimakin ƙaramar hukuma zuwa sahun gaba na manyan ‘yan siyasar Jihar Kano.
An haifi Garo a ranar 16 ga Mayu, 1978, a garin Garo da ke Ƙaramar Hukumar Kabo. Ya taso a gida mai daraja da ke koyar da mutunci, hidima da haɗin kai. Waɗannan darussa na farko ne suka gina tunaninsa na siyasa bisa akidar cewa ci gaba mai tasiri dole ne ya fara daga tushe, wato matakin al’umma.
Yayin da yake tasowa, Garo ya shiga aikin gwamnati a matsayin Mai Ba da Shawara na Musamman ga Shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo. A nan ne halayen jagorancinsa suka fara bayyana, inda kwarewarsa wajen fassara bukatun al’umma zuwa ayyuka masu amfani ta sa aka zaɓe shi Shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo.
Da ya zama Shugaban Kabo LGA, abokan aikinsa sun gane ƙwazon jagorancinsa. A cikin ƙananan hukumomi 44 na jihar, aka zaɓe shi ya shugabanci Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomi ta Najeriya (ALGON) reshen Kano.
A matsayinsa na Shugaban ALGON, ya tabbatar da kyakkyawar alaƙa mai ɗorewa tsakanin gwamnatin jiha da ƙananan hukumomi, lamarin da ya taimaka wajen hanzarta ci gaba da kuma cin gajiyar albarkatun jihar yadda ya kamata.
Daga shekarar 2019 zuwa 2023, Garo ya riƙe muƙamin Kwamishinan Harkokin Ƙananan Hukumomi da Masarautu. A wannan lokaci, ya kasance jigon ajandar bunƙasa karkara a Kano, inda aikinsa ya ta’allaka ne kan ginshiƙai uku masu muhimmanci:
– farfaɗo da ilimi ta hanyar gyaran makarantu na firamare a dukkan ƙananan hukumomi 44;
– bunƙasa ababen more rayuwa a karkara don buɗe sabbin hanyoyin kasuwanci ga manoma da ƙarfafa tattalin arziki;
– aiwatar da shirye-shiryen da suka rage ƙaurace-ƙauracen karkara zuwa birane ta hanyar fitar da jama’a daga talauci.
Salon aikinsa na kai-tsaye da fahimtar aiki ya ba shi suna a matsayin “mai aiwatarwa” ba mai magana kawai ba, lamarin da ya ba shi kima har ma a tsakanin ‘yan jam’iyyun adawa.
Masu ruwa da tsaki a jam’iyya suna bayyana Garo a matsayin “injin siyasa” mai iya tara ƙuri’u a birane da karkara. Tare da tarihin nasarori, tushensa mai ƙarfi a Mazabar Sanatan Arewa ta Kano da tasirinsa a ƙungiyoyin matasa, hakan ne ya sa aka zaɓe shi bisa dabaru a matsayin mataimakin takarar gwamna ga Dr. Nasir Yusuf Gawuna a zaɓen 2023.
Salon jagorancinsa—wanda ake bayyana shi a matsayin haɗin tsari irin na soja da tausayi na farar hula—yana saita manufofi a fili tare da kasancewa kusa da jama’a, mai tawali’u da sauƙin samu. Yana ba da aiki amma yana bibiyar sakamako da kansa, abin da ya ƙara ƙarfafa laƙabinsa na “Commander.”
Hanyar Gaba
Yayin da Kano ke shirin shiga wani gagarumin sauyin siyasa, Murtala Sule Garo ya tsaya a matsayin mafi dacewa kuma mai yiwuwa don muƙamin Mataimakin Gwamna. Tarihinsa na aiki na nuna zai fifita ci gaban karkara mai ɗorewa, saka hannun jari a jarin ɗan Adam, da shugabanci na gaskiya.
Ta hanyar naɗa Garo, Gwamna Abba Kabir Yusuf na da wata dama ta musamman wajen ƙarfafa gwamnatinsa a yanzu da kuma haskaka damar sake lashe zaɓe a 2027. Haɗuwar amincewar jama’a a matakin ƙasa-ƙasa da ƙwarewar gudanarwa da Garo ke da ita na sa ya zama muhimmin jigo wajen tsara makomar Jihar Kano.
