Politics

AMATA TA KAI ZIYARAR BANGIRMA DA JADDADA GOYON BAYANTA GA GWAMNA ABBA

IMG 20260211 WA0001
IMG 20260211 WA0001

AMATA Ta Ziyarci Kwamishina Waiya, Ta Sake Jaddada Goyon Baya ga Gwamna Abba Kabir Yusuf

Shugabanni da mambobin Ƙungiyar Nigerian Amalgamated Traders and Artisans Welfare Development Association (AMATA), ƙarƙashin jagorancin Shugabanta, Alhaji Abdul’aziz Dalha Musa, a ranar Talata, 10 ga Fabrairu, 2026, sun kai ziyarar girmamawa ga Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, domin nuna haɗin kai da goyon bayansu ga Mai Girma Gwamnan Jahar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf.

IMG 20260210 WA0322 768x509

A yayin ziyarar, ƙungiyar ta sake tabbatar da amincewarta da jagorancin Gwamnan tare da yin alƙawarin ci gaba da mara wa gwamnatin baya wajen aiwatar da shirye-shiryen bunƙasa jihar Kano. Haka kuma, sun jaddada shirinsu na ganin ‘yan kasuwa da masu sana’o’i sun taka rawar gani wajen samar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da bunƙasar tattalin arzikin jahar Kano.

AMATA ta ƙara jaddada aniyarta ta tara cikakken goyon baya ga Gwamna Abba Kabir Yusuf domin tabbatar da ci gaba da tafiyar da gwamnati, saboda dorewar zaman lafiya, ci gaba da habakar tattalin arziki.

A nasa martanin, Kwamishina Waiya ya sanar da tawagar cewa matakin siyasar da Gwamnan ya ɗauka na komawa jam’iyyar APC ya samo asali ne daga muradun al’ummar jahar Kano gaba ɗaya, da kuma buƙatar ƙarfafa ayyukan ci gaba da ake gudanarwa. Ya bayyana manyan ayyuka da ake aiwatarwa a ƙananan hukumomi 44 a matsayin hujja ta ƙudirin gwamnatin wajen inganta rayuwar jama’a da faɗaɗa damammaki, musamman ga matasa.

Kwamishinan ya tabbatar wa ƙungiyar cewa ‘yan kasuwa da masu sana’o’i muhimman abokan hulɗa ne a ajandar ci gaban jihar, tare da ƙara da cewa manufofin da ke nufin ƙarfafa harkokin kasuwanci za su ci gaba da samun kulawa ta musamman.

Ya yaba wa AMATA bisa ƙudurinta da ziyarar haɗin kai da ta kawo, tare da nuna godiya ga sabunta goyon bayan da ƙungiyar ta nuna wa Gwamna Abba Kabir Yusuf da kuma jajircewarta wajen haɗa kai domin bunƙasa muradun al’ummar jihar Kano.

Sa hannu:

Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida

10 ga Fabrairu, 2026

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *